Kalaman Trump sun raba kan 'yan Republican

Wannan shafin na kawo muku labarai da rahotanni kai tsaye kan zaben Amurka da ma abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Rahoto kai-tsaye

Imam Saleh and Mustapha Musa Kaita

  1. Rufewa

      • Marubuci, Mustapha Musa Kaita
      • Sanya sunan wanda ya rubuta labari, Multi-Media Broadcast Journalist

    Masu bibiyarmu a wannan shafin a nan muka zo ƙarshen kawo muku labarai da rahotanni kai tsaye, sai kuma gobe Asabar idan Allah ya kai mu za mu ci gaba da kawo muku wasu labaran.

    Ga wasu daga cikin labaran da muka wallafa a wannan shafin:

    • Afrika Ta Kudu ta fara tasa ƙeyar 'yan ci-ranin da suka fito daga ƙasashen Afrika
    • Za a sake ƙirga ƙuri'u a Georgia
    • Ali Ƙwara Azare 'mai kama ɓarayi' ya rasu
    • Amurka ta saka wa surukin shugaban Lebanon takunkumi
    • Buhari ya karɓi rahoton abubuwan da suka faru bayan rikicin ENDSARS a Legas
    • An samu 'ƙaruwar' fashi da makami a Jihar Edo

    Za ku iya duba ƙasa domin karanta waɗannan labaran da ma wasu muhimmai.

  2. Kalaman Trump sun raba kan 'yan Republican

    .

    Asalin hoton, Reuters

    Shugabar Jam'iyyar Republican a Amurka, Ronna McDaniel, ta bayyana cewa har yanzu faɗa bai ƙare ba, haka kuma tuni aka tura lauyoyi zuwa jihohi huɗu domin gudanar da bincike kan abin da ta kira "aikata ba daidai ba".

    Sai dai iƙirarin da Trump ɗin ke yi na magudin zaɓe wanda bai kawo hujja ba ya raba kan 'yan jam'iyyarsa.

    Domin kuwa, a wata sanarwa da Sanata Mitt Romney ya fitar a Twitter, ya bayyana cewa Mista Trump na da 'yancin buƙatar a sake ƙirga ƙuri'u, amma ba daidai bane ya ce an yi maguɗi a zaɓen ba ko kuma cin hanci ko an masa sata.

    Haka shi ma Pat Toomey, wanda sanata ne kuma daga Jihar Pennsylvania, ya bayyana cewa zargin da Trump ɗin ke yi na almundahana bai da wani tushe, haka kuma Mista Tommey din ya ce bai da wata masaniya kan wani ba daidai da aika aikata ba.

  3. Ana binciken jagororin 'yan adawa uku a Ivory Coast

    Hukumomi a Ivory Coast, sun bayyana cewa ana gudanar da bincike kan wasu jagorori uku daga ɓangaren adawa bisa zarginsu da tawaye da ta'addanci da kuma watsi da zaɓen Shugaba Alassane Ouattara inda suka sha alwashin kafa gwamnati.

    Mutane ukun sun haɗa tsohon firaiministan ƙasar Pascal Affi N'Guessan, wanda a yanzu ba a san inda yake ba.

    Akwai kuma babban abokin hamayyar Mista Ouattara, wato tsohon shugaban ƙasa Konan Bedie, wanda mai gabatar da ƙara a ƙasar ya ce tuni 'yan sanda sun toshe ƙofar shiga gidansa.

    Aƙalla mutum 40 aka kashe a rikici da kuma arangama da aka rinƙa samun tun a Agustan 2020, wanda hakan ya saka fargabar cewa Ivory Coast za ta iya faɗawa cikin yaƙi bayan zaɓe, kamar yadda hakan ya faru shekaru 10 da suka gabata inda aka kashe mutum dubu uku.

  4. Amurka ta saka wa surukin shugaban Lebanon takunkumi

    ...

    Asalin hoton, Reuters

    Baitul malin Amurka, ta ƙakaba takunkumi kan wani babban ɗan siyasa a Lebanon, Gebran Bassil, bisa zarginsa da hannu a aikata cin hanci da rashawa.

    Mista Bassail dai tsohon ministan harkokin waje ne kuma jagoran jam'iyyar siyasa ta Kirista da ke ƙawance da Kungiyar Hezbollah ta ’yan Shi'a.

    Haka kuma, suruki ne ga Shugaban Lebanon Michel Aoun.

    Sai dai Mista Bassil ya ce takunkumin da aka ƙaƙaba masa bai ba shi tsoro ba sannan ya saɓa da abin da ya kira rashin adalci.

  5. MINTI ƊAYA DA BBC - LABARAN YAMMA 06/11/20

    Bayanan sautiLatsa alamar lasifikar da ke sama domin sauraren labaran
  6. 'Yan Twitter sun fusata kan yunƙurin ba jami'an Road Safety bindiga a Najeriya

    ..

    Asalin hoton, Google

    'Yan Najeriya da dama sun fusata a shafukan sada zumunta musamman a Twitter tun bayan ɓullar wani labari da ake yaɗawa kan cewa za a fara bai wa jami'an hukumar kiyaye haɗura ta Najeriya bindigogi.

    Jaridar Daily Post a Najeriya ta ruwaito shugaban kwamitin hukumar ta FRSC a Majalisar Wakilai, Akinfolarin Mayowa, inda ya ce ya zama tilas a yi hakan domin tabbatar da an bi doka da oda.

    Ya bayyana hakan ne yayin da hukumar ta hallara gaban kwamitin na majalisar domin kare kasafin kuɗinta na 2021 da ta gabatar.

    Ga cikakken labarin a nan:

  7. Buhari ya karɓi rahoton abubuwan da suka faru bayan rikicin ENDSARS a Legas

    .

    Asalin hoton, Nigeria Presidency

    Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya karɓi baƙuncin Gwamnan Legas, Babajide Sanwo-Olu a fadar shugaban ƙasar da ke Abuja.

    Shugaban ƙasar ya tattauna da gwamnan kuma ya karɓi kundin rahoton abubuwan da suka faru bayan zanga-zangar ENDSARS da ta haddasa asarar biliyoyin nairori a jihar.

    Ƙididdiga ta bayyana cewa an yi asarar sama da naira biliyan 400 sakamakon ƙone-ƙonen da aka yi da lalata kadarori a jihar.

    An lalata sama da ofisoshin 'yan sanda 205 da kashe sama da 'yan sanda 20.

    Ga wasu daga cikin manyan wuraren da aka kai wa hari

    • Hedikwatar hukumar kula da tashoshin jiragen ruwa ta Najeriya, NPA
    • Gidan Oba na Legas
    • Gidan talabijin na TVC
    • Gidan mahaifiyar Gwamna Sanwo-Olu
    • Tashar mota ta Oyingbo
    • Otel din Orientel
    • Ofishin hukumar Road Safety da VIO
    • Babbar Kotun da ke Igbosere
    • Manyan kantunan sayar da kayayyaki na Shoprite da Spar
    • Ofishin jaridar The Nation
    ..

    Asalin hoton, Nigeria Presidency

  8. Tazarar da Biden ya ba Trump a Jihar Arizona ta ragu

    Tazara mai tsawo da Biden ya bai wa Trump a Jihar Arizona na ƙara raguwa.

    A halin yanzu, Mista Biden na gaban Trump da ƙuri'a 43,570 a jihar, wanda a baya yana gabansa da ƙuri'a 47,000.

    Ana ci gaba da kirga ƙuri'u a yankin Maricopa, wanda shi ne yanki mafi girma a jihar, kuma an bayar da rahoton an kaɗa kusan kuri'a miliyan biyu a yankin, wanda hakan ke nufin kashi 75 cikin 100 na 'yan yankin sun yi zaɓe.

    Yankin na Maricopa na cewa akwai kusan ƙuri'u 142,000 da har yanzu ba a ƙirga ba.

  9. An samu 'ƙaruwar' fashi da makami a Jihar Edo

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Rahotanni daga Jihar Ondo na cewa ana samun yawaitar 'yan fashi da makami a jihar.

    Wasu na ganin hakan ba zai rasa nasaba da ƙarancin jami'an tsaro akan titunan jihar.

    'Yan jihar sun shaida wa BBC cewa a baya ana samun fashi da makami jefi-jefi, amma a halin yanzu, sai kiyayewar Allah.

    Wasu na cewa aƙalla ana samun fashi da makami a jihar aƙalla sau 10 a rana, sai dai a tattaunawar da BBC ta yi, da rundunar 'yan sandan jihar, ta ce ana samun fashi da makami amma ba su da labarin cewa fashi da makamin ya ƙaru sosai.

    Rundunar ta ce a baya bayan nan ta kama wasu da ake zargi 'yan fashi da makami ne da bindigogi da harsasai da miyagun makamai.

  10. Ali Ƙwara Azare 'mai kama ɓarayi' ya rasu

    Ali Ƙwara

    Asalin hoton, Nazif Babaji

    Allah Ya yi wa fitaccen mutumin nan mai kama ɓarayi a Najeriya Ali Ƙwara Azare rasuwa a yau Juma'a.

    Ali Ƙwara ya rasu ne a Abuja bayan ya sha fama da jinya.

    Ya rasu ya bar mace daya da ƴaƴa huɗu sai kuma ƴan uwa masu ɗan dama.

    Marigayin haifaffen Azare ne da ke ƙaramar hukumar Katagum a jihar Bauchi.

    Ya yi fice sosai wajen kama ɓarayi a dazuzzukan, sannan daga bisani ya ladabtar da su da kuma koya musu sana'o'i.

    Ƴan uwansa sun sanar da cewa za a yi jana'izarsa a garin Azare.

  11. Za a sake ƙirga ƙuri'u a Georgia

    Sakataren harkokin wajen Jihar Georgia ta Amurka, Brad Raffensberger, ya bayyana cewa za a sake ƙidaya ƙuri'un jihar da aka kaɗa.

    Ya bayyana cewa akwai sauran ƙuri'u 4,169 da ya kamata a ƙirga, haka kuma akwai kuri'un sojoji 8,000 da aka aika ta gidan waya da ba a kirga ba, kuma za a ƙirga su ne kawai idan sun iso.

    Ya bayyana cewa ƙuri'un da za a ƙirga na Georgia na da muhimmanci ga zaɓen Amurka baki ɗaya.

    Sterling, wanda shi ke sa ido kan zaɓe a jihar, ya bayyana cewa dalilin da zai sa asake kirga ƙuri'un shi ne yadda ake tafiya kan-kan-kan a zaɓen, haka kuma a cewarsa, babu wasu abubuwan da aka aikata da ba daidai ba da ke kama da maguɗi.

  12. Ku San Malamanku: tare da Shiekh Abduljabbar Nasiru Kabara

    Bayanan bidiyo, Latsa alamar hoton da ke sama domin kallon bidiyon
  13. Afrika Ta Kudu ta fara tasa ƙeyar 'yan ci-ranin da suka fito daga ƙasashen Afrika

    ..

    Asalin hoton, AFP

    Ma'aikatar harkokin cikin gida ta Afrika Ta Kudu ta bayyana cewa ta fara tasa ƙeyar 'yan ci-rani 20, akasarinsu daga ƙasashen Afrika waɗanda ke cikin mutanen da suka yi zanga-zangar ƙin jinin baƙi.

    An fara zanga-zangar ne tun a watan Oktoban 2019 a Cape Town, inda aka yi zaman dirshen a gaban ofisoshi n hukumar kula da 'yan gudun hijira ta Majalisar Ɗinkin Duniya.

    Masu zanga-zangar na so ne su bar Afrika Ta Kudu su koma wata ƙasa, amma ba su so su koma ƙasar su ta asali.

    'Yan ci-ranin sun bayyana cewa ana musguna musu da kuma nuna musu wariya, wanda hakan ya sa suke ji ba su da wani tsaro a tattre da su a biranen ƙasar.

    Ma'aikatar harkokin cikin gida ta ƙasar ta bayyana cewa an bi ka'ida wajen tasa ƙeyar 'yan ci-ranin 20, kuma sai da kotu ta ba su izinin yin hakan.

    Ana sa ran za a ci gaba da tasa ƙeyar wasu ayarin 'yan ci-ranin.

  14. An saki malamin addinin kiristan da aka sace a Kamaru

    Malamin da aka sace

    Asalin hoton, Getty Images

    Mutanen da suka sace malamin addinin kiristan nan na Kamaru wato Christian Tumi sun sake shi a yau.

    Kwana ɗaya tak ya shafe a hannunsu.

    An sace malamin Tumi wanda a lokuta da dama yake neman shiga tsakani a rikicin da aka shafe shekara uku ana yi tare da wasu mutum 10 yayin da suke tuka mota daga Yaounde babban birnin kasar zuwa garin Kumbo.

    Daga cikin mutanen da aka sace har da wani basaraken gargajiya.

    Akwai rahotannin da ke cewa mutane da dama sun yi tattaki zuwa sansanin 'yan awaren domin neman a saki wadanda aka yi garkuwa da su.

    Ƴan awaren yankin renon Ingila da ke Kamaru sun sha yin garkuwa da mutane kuma galibi domin neman kudin fansa.

  15. Labarai da dumi-dumi, Biden ya wuce gaba a Pennsylvania

    Biden

    Asalin hoton, AFP

    Dan takarar shugaban Amurka a jam'iyyyar Democrat Joe Biden ya wuce gaba wajen yawan ƙuri'u a jihar Pennsylvania.

    Ya wuce gaba da ƙuri'a dubu biyar da dari biyar da tamanin da bakwai, yayin da aka kammala ƙirga kashi 95 cikin 100 na ƙuri'un da aka kaɗa a jihar baki ɗaya.

    Yana dab da samun ƙuri'un wakilan masu zaɓe 270 da za su bashi damar zama shugaban Amurka.

  16. Ƴan sanda a Jamus sun bazama don neman maharin da ya kai harin Vienna

    'Yan sandan Jamus

    Asalin hoton, Getty Images

    'Yan sandan Jamus na gudanar da samame a birane uku dangane da harin da aka kai a Vienna, babban birnin Austria.

    A ranar Litinin din da ta gabata ne wani mai da ake kyautta zaton mai ikirarin jihadi ne ya halaka mutum hudu.

    Ofishin 'yan sanda da ke kula da manyan laifuka ya ce ba a tunanin mutane hudun da ake nema suna da alaka ta kai tsaye da dan shekara 20 din da ake zargi da kai harin wanda kuma tuni yan sanda suka harbe shi.

    Tuni dai ƴan sandan Austria suka kama mutum 15 da suke cikin kungiyoyi masu tsatsatsauran ra'ayi.

  17. An hana wata jagorar zanga-zangar EndSars fita daga Najeriya a filin jirgi

    endsars

    Asalin hoton, AFP

    Hukumar shige da fice ta Najeriya ta ce ta ƙwace fasfo ɗin wata fitacciyar mamba da ke gaba-gaba a zanga-zangar EndSars da aka yi kwanan nan a ƙasar.

    Ta ce an ƙwace fasfo ɗin Modupe Odele ne a yayin da take kan hanyarta ta tafiya hutu,a lokacin da ake gudanar da bincike a kanta.

    Ms Odele ta tsaya wa ɗaruruwan masu zanga-zanga irin tsayawar shari'a, tare da haɗo kan lauyoyi 800 da suka taimaka wajen samar da belin waɗanda aka kama.

    Zanga-zangar ta kawo ƙarshe ne bayan da aka buɗe wuta kan gomman masu yin ta a unguwar Lekki ranar 20 ga watan Oktoba a Legas.

  18. Ƴan aware sun yi garkuwa da malamin addinin kirista a Kamaru

    Kamaru

    Ƴan aware a Kamuru sun yi garkuwa da wani malamin addinin kirista a arewa maso yammacin kasar.

    An sace malamin Tumi wanda a lokuta da dama yake neman shiga tsakani a rikicin da aka shafe shekara uku ana yi tare da wasu mutum 10 yayin da suke tuka mota daga Yaounde babban birnin kasar zuwa garin Kumbo.

    Daga cikin mutanen da aka sace har da wani basaraken gargajiya.

    Akwai rahotannin da ke cewa mutane da dama sun yi tattaki zuwa sansanin 'yan awaren domin neman a saki wadanda aka yi garkuwa da su.

    Ƴan awaren yankin renon Ingila da ke Kamaru sun sha yin garkuwa da mutane kuma galibi domin neman kudin fansa.

    A ranar Alhamis ne aka saki malamai 11 bayan da aka yi garkuwa da su a wata makaranta a farkon makon nan.

  19. Abin da ke faruwa dangane da zaben Amurka a takaice

    Idan yanzu-yanzu kuka shigo shafin to ga abin da ke fatruwa a takaice dangane da zaben Amurka:

    Har yanzu muna dakon sanar da wanda ya yi nasara a zaen Amurka na 2020.

    A yanzu dai dan takarar Democrat Joe Biden ne ya fi alamun nasara. A lokaci guda kuma Donald Trump ya yi zargin cewa an yi magudi a zaben duk da dai bai bayar da hujjoji ba.

  20. Masu zanga-zangar End SARS sun yi arangama da ƴan sanda a Abuja

    Masu zanga-zanga

    Asalin hoton, OTHERS

    Jami'an tsaro a Abuja sun yi arangama da masu zanga-zangar End SARS, abin da ya janyo tsare wasu daga cikinsu.

    Masu zanga-zangar da suka taru a majalisar wakilan ƙasar na neman hukumomi su yi garambawul ga tsarin aikin ƴan sanda, sakamakon zargin da ake yi musu na zaluntar jama'a.

    Jaridar This Day ta rawaito cewa ƴan sandan sun yi harbi a sama.

    Wani ɗan gwagwarmaya Omoyele Sowere ne ya jagoranci zanga-zangar da ta haifar da cunkoson ababen hawa a titin Shehu Shagari da ke birnin na Abuja.